Bajoga | ||||
---|---|---|---|---|
| ||||
Wuri | ||||
| ||||
Yawan mutane | ||||
Harshen gwamnati | Turanci |
Bajoga gari ne kuma hedikwatar karamar hukumar Funakaye dake jahar Gombe a Arewa maso Gabashin Najeriya.[1] Bajoga ta kasance garine dake da nisan kilomita tara daga Ashaka inda ananne ma'aikatar da'ake sarrafa siminti take.
Sannan kuma tana da nisan kilomita daya daga Bormi, tsohon garin da akayi yaki tsakanin turawan mulkin mallaka na Burtaniya da kuma Sarkin Musulmi na wancan Zamanin, Muhammadu Attahiru l. Wanda yayi gudu daga Sokoto zuwa wannan yankin harkuma aka kasheshi a shekarar 1903.